Isa ga babban shafi
Somalia

An fara makokin kwanaki 3 a Somalia

Gwamnatin Somaliya ta sanar da makokin kwanaki 3 bayan tagwayen hare-haren kunar bakin waken da aka kai birnin Mogadishu a jiya da ya hallaka akalla mutane 137.

Zaman makokin na kwanaki 3 na zuwa ne a dai dai lokacin da adadin mutanen da tagwayen hare-haren kunar bakin waken da aka kai birnin Mogadishu ya haura mutum 200.
Zaman makokin na kwanaki 3 na zuwa ne a dai dai lokacin da adadin mutanen da tagwayen hare-haren kunar bakin waken da aka kai birnin Mogadishu ya haura mutum 200. REUTERS/Feisal Omar
Talla

A cewar shugaba Muhammad Abdullahi Muhammad Farmaajo za a fara makokin daga yau Lahadi don nuna alhini ga mutanen da suka rasa rayukansu.

Kawo yanzu akwai sama da mutane 250 da ke karbar kulawar gaggawa a asibitoci bayan samun munanan raunuka sanadiyyar harin na jiya.

Wannan dai shi ne mafi munin hari da aka kai birnin na Mogadishu cikin shekarun nan, inda a bangare guda kuma shugaba Muhammad ya bukaci al’umma su tallafawa mutanen da harin ya rutsa da su.

Har ya zuwa yanzu dai babu wata kungiya da ta yi ikirarin kai harin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.