Jami'an tsaron Libya sun dakile yunkurin masu safarar bakin-haure
Jami’an tsaron Libya da hadin gwiwar wasu jiragen ruwan bada agaji na kasa da kasa, sun yi nasarar katse yunkurin gungun masu safarar mutane da ke kokarin ketarar da daruruwan bakin-haure zuwa Italiya daga Libya.
Wallafawa ranar:
Kakakin jami’an tsaron gabar ruwan na Libya Ayoub Qassem ya ce jirage uku na masu safarar suka samu nasarar katsewa hanzari, kuma bakin-haure 125 ke cikin jirgin ruwa na farko.
Jirgi na biyu kuwa yana dauke ne da bakin haure 98, yayin da jirgi na uku da aka tsare yake dauke da bakin-haure 100, wadanda ake shirin tsallaka tekun Mediterranean da su zuwa kasar Italiya.
‘Yan Najeriya 50 ne ke cikin bakin-hauren da aka ceto daga tekun na Mediterranean, da ke cikin jiragen ruwan da ke kokarin tsallkar da su zuwa Italiya.
Sama da bakin-haure dubu 600,000 suka ketara tekun Mediterranean zuwa Italiya cikin shekaru 4, yayinda wasu dubbai suka hallaka a cikin teku.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu