Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Congo

Sama da 'yan Jamhuriyar Congo 57,000 sun tsere zuwa Uganda

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, ta ce sama da ‘yan kasar Jamhuriyar Congo 57,000 sun tsere zuwa makwabciyar su Uganda a cikin wannan shekara.

Wasu daga cikin dubban 'yan Jamhuriyar congo da ke tserewa zuwa Uganda, ta hanyar tsallaka tafkin Albert da jiragen ruwa na kwale-kwale.
Wasu daga cikin dubban 'yan Jamhuriyar congo da ke tserewa zuwa Uganda, ta hanyar tsallaka tafkin Albert da jiragen ruwa na kwale-kwale. AFP / JOHN WESSELS
Talla

Hukumar ta ce adadi ya zarta na shekarar bara ta 2017, inda ‘yan kasar sama da 44,000 suka tsere zuwa Ugandar.

Dubban ‘yan kasar ta Jamhuriyar Congo na gujewa rikicin kabilanci ne musamman inda ya yi kamari a lardin Ituri da ke arewa maso gabashin kasar.

Ana gwabza kazamin rikicin ne tsakanin manoma na kabilar Lendu da kuma makiyaya na kabilar Hema akan mallakar filaye, kuma zuwa yanzu an hallaka mutane 130 daga dukkanin bangarorin, tun bayan sake tashin rikici tsakaninsu a watan Disambar bara, lamarin da ya raba mutane 20,000 da muhallansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.