Buhari zai dawo Najeriya a yammacin yau
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari na kan hanyar sa ta dawowa gida a yammacin yau Alhamis bayan ziyarar da ya kai Kasar Amurka bisa gayyatar shugaban kasar Donald Trump.
Wallafawa ranar:
Mai magana da yawun shugaban Najeriyar Mr Femi Adesina ya ce a yammacin yau ne Muhammadu Buhari zai iso Najeriya bayan wani tsaiko da jirginsa ya fuskanta wanda ya tilasta masa tsayawa a Birnin London na kasar Birtaniya.
Sanarwar ta Mr Femi Adesina ta kawo karshen tantamar da ake da ita kan abin da ya tsayar da shugaban a birnin London kwanaki biyu bayan barowarshi Amurka ranar Talata.
A safiyar yau ne dai mataimakin shugaban Najeriyar na musamman kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ya ce wani tsaiko ne ya tsayar da shugaban a birnin London.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu