Isa ga babban shafi
Najeriya-Boko Haram

Mutane da dama sun mutu a harin da Boko Haram ta kai Gundumbali

Ana fargabar mutane da dama sun rasa rayukansu bayan wani hari da mayakan boko haram suka kai kauyen Gundumbali da ke wajen birnin Maiduguri na jihar Borno a yankin arewa maso gabashin Najeriya yau Asabar.

Kawo yanzu dai babu hakikanin adadin mutanen da suka mutu a harin ko da dai wani mazaunin garin ya ce akwai tarin fararen hula da suka rasa rayukansu.
Kawo yanzu dai babu hakikanin adadin mutanen da suka mutu a harin ko da dai wani mazaunin garin ya ce akwai tarin fararen hula da suka rasa rayukansu. RFI/OR
Talla

Rahotanni sun ce mayakan na Boko Haram sanye da kayan soji sun yiwa garin na Gudumbali tsinke yayinda suka fara harbi kan jami’an sojin da ke bayar da tsaro ga garin matakin da ya tilastawa sojin hade da fararen hula tserewa don tsira da rayukansu.

A watan Yunin daya gabata ne gwamnatin Najeriyar ta yi umarnin mayar da al’ummar garin na Gudunbula da ke yankin Guzamala matsugunansu la’akari da yadda ake samun nasara kan kungiyar ta Boko haram da ta addabi yankin.

Wani mazaunin garin da aka bayyana sunanshi da Muhammad ya ce kawo yanzu basu kayyade adadin mutanen da suka mutu a harin ba, ko da dai rundunar sojin ta Najeriya ta haramta musu magana da manema labarai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.