Shekarau ya tabbatar da komawarsa APC daga PDP
Tsohon gwamnan jihar kano Ibrahim Shekarau wanda ke matsayin jigo a Jam’iyyar adawa ta Najeriya PDP ya sanar da kammala komawarsa jam’iyyar APC mai mulkin kasar yau Asabar.
Wallafawa ranar:
Ibrahim Shekarau wanda ya tsaya neman kujerar shugabancin Najeriya a 2011 ya sanar da komawar ta sa APC ne a hukumance yau Asabar yayin wani taro dfa ya yi da magoya bayansa a gidansa da ke Mundubawa a jihar ta Kano.
A cewarsa ya sauya shekar ne sakamakon rashin adalcin da ya ke fuskanta a PDP musamman kan abin da ya shafi shugabancin jiha wanda ya mayar da shi da magoya bayansa saniyar ware.
Sai dai yayin ayyana komawar APC na Shekarau ba a ga wasu daga cikin jiga-jigan magoya bayansa da suka kunshi Salihu Sagir Takai ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu