Al'ummar Senegal na kada kuri'a a zaben shugaban kasa
Yau Lahadi, al’ummar Senegal ke kada kuri’a a zaben shugabancin kasar, bayan kawo karshen yakin neman zaben ‘yan takara a ranar Juma’ar da ta gabata.
Wallafawa ranar:
Yan takara 5 ne za su fafata a zaben shugabancin na Senegal, cikinsu har da shugaba mai ci Macky Sall, yayinda ake sa ran ‘yan kasar akalla, miliyan 6 da dubu 500 za su kada kuri’a.
Karo na farko kenan da zaben shugaban kasa zai gudana a Senegal bayan zaben raba gardama na shekarar 2016, wanda ya bada damar rage yawan shekarun da shugaba zai shafe bisa mulki daga shekaru 7 mai tsarin wa’adi daya, zuwa shekaru 5 bisa tsarin wa’adi guda biyu.
Daga cikin ‘yan takarar 5 da za su fafata, Ousmane Sonko mai shekaru 44 ne mafi kankanta a cikinsu, wanda kuma ya sha alwashin sake nazari kan kwagilolin manyan ayyuka da gwamnatin Senegal da baiwa wasu kamfanonin Faransa, muddin yayi nasarar lashe zaben.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu