Ana fargabar mutuwar kananan yara bayan ruftawar bene mai hawa 3 a Lagos
Rahotanni daga jihar Lagos a Najeriya na cewa akalla kananan yara 10 ake fargabar sun makale a baraguzan gine-gine bayan rugujewar wani gini mai hawa 3 a unguwar Itafaji da ke jihar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar wadda ta tabbatar da faruwar lamarin ta ce yanzu haka ana ci gaba da aikin ceton kananan yaran da suka makale a ginin.
A cewar Ibrahim Farinloye kakakin yada labaran hukumar agajin gaggawar ya ce makarantar ita ce hawan karshe na ginin benen mai hawa 3, yayinda ake fargabar mutuwar kananan yara.
Rugujewar gine-gine masu tsayi dai ba sabon abu ba ne a Najeriya don ko a watan Satumban 2014 ma akalla mutane 116 ne suka mtu bayan fadowar wani gini mai hawa 6 a jihar ciki har da 'yan kasar Afrika ta kudu 84, wanda daga bisani kuma aka gano cewa an yi ginin ne ba bisa ka'ida ba.
Ka zalika ko a watan Disamban 2016 ma wani ginin Majami'a da ya ruguzo a jihar Uyo da ke kudancin Najeriyar ya hallaka mutane 60.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu