Isa ga babban shafi
Mali

An fitar da tsohon shugaban Mali zuwa Hadaddiyar Daular Larabawa

Tsohon shugaban ma’aikatan fadar hambararren shugaban Mali Ibrahim Boubacar Kieta, Mamadou Kamara yace an fita da tsohon shugaban kasar zuwa birnin Abu Dhabi a Hadaddiyar Daular Larabawa a jiya asabar, domin kulawa da lafiyarsa.

Tsohon Shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita
Tsohon Shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita Ludovic Marin /Pool via REUTERS
Talla

Tun Talatar makon da ya kare ne dai aka kwantar da tsohon shugaba Kieta a wani asibiti dake birnin Bamako, kwanaki 6 bayan sakinsa da sojin kasar suka yi daga tsarewar da suka masa, ranar 18 ga watan Agusta, lokacin da suka yi juyin mulki.

A jiya asabar din kuma aka soma tattaunawa tsakanin gwamnatin sojin na Mali da wakilan jam’iyyu da sauran kungiyoyin a birnin Bamako, kan shirin sake mikawa farar hula mulki.

Sai dai rahotanni sun ce sa’o’i kalilan bayan soma ganawar gamayyar kungiyar ‘ayn adawa ta M5-RFP da ta soma jagorantar zanga-zangar kin jinin tsohon shugaba Kieta, ta zargi gwamnatin sojin kasar ta maida ta saniyar ware a tattaunawar da ta soma da farar hula, abinda ya sanya ta kaddamar da wata sabuwar zanga-zangar, matakin da ya tilasta dakatar da taron na wucin gadi.

Yau alahadi taron sojin da farara hular na Mali ke cigaba da gudana, zalika za a dora kansa a sassan kasar cikin mako mai kamawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.