Isa ga babban shafi
G5 Sahel - Nijar

An kammala taron kasashen G5 Sahel a birnin Yamai

An kawo karshen taron kasashen G5 sahel a birnin Yamai ta Jamhuriyar Nijar, bayan da aka kwashe kwanaki biyu ana tauttanawa a kan yadda za’a yi a shawo kan matsalolin tsageranci da ta’addanci a yankin tsakiyar sahel da wuraren tafkin Chadi.

Taron tattauna matsalolin tsaro da suka addabi yankin Sahel ya gudana ne a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar.
Taron tattauna matsalolin tsaro da suka addabi yankin Sahel ya gudana ne a birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar. AFP - MICHELE CATTANI
Talla

Domin shawon kan matsalolin tsaro da suka addabi yankin tsakiyar sahel da tafkin Chadi ne hukumar karfafa zaman lafiya HACP ta Nijar, tare da hadin gwiwar kungiyar PNUD suka gudanar da wani taron nazari a birnin Yamai.

Taron ya samu halartar manyan masana kan zaman lafiya, kuma shugaban taron, Janar abou Tarka ya ce an cimma biyan bukata a taron.

sai dai wasu matasa da suka samu lekawa zauren taron sun koka da yadda ba a ba su damar kawo tasu fusahar ba sakamakon rashin gayyatar su a hukumance.

Taron ya yi Nazari kan abubuwa uku da ke da nasaba da tsaro, kuma za a mika su ga gwamnatoci a  matsayin shawarwari da za su taimaka wajen kawo karshen  ta’addanci a yankin tsakiyar sahel da tafkin chadi.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.