Isa ga babban shafi
Algeria - France 24

Algeria ta soke lasisin France 24

Algeria ta soke lasisin da ke bai wa wakilan tashar talabijin ta France 24 damar gudanar da ayyukanta a cikin kasar.

Tambarin kafar Talabijin ta France 24.
Tambarin kafar Talabijin ta France 24. ALEXANDER KLEIN AFP/File
Talla

Sanarwa da ma’aikatar watsa labaran Algeria ta fitar a marecen jiya lahadi, ta ce an dauki matakin ne lura da yadda ta nuna son-kai wajen yada zanga-zangar masu hamayya da gwamnatin kasar.

Sai dai France Media Monde, da ke matsayin shugabar rukunin kafafen yada labaran Faransa masu watsa shirye shirye zuwa kasashen ketare ta bayyana mamaki kan matakin da gwamnatin Algerian ta dauka.

A baya bayan nan kungiyar ‘yan jaridu ta duniya RSF ta sanya Algeria a matsayi na 146 daga cikin kasashe 180 da suke mutunta aikin jarida da fadin ‘yancin albarkacin baki.

Masu zanga-zangar neman sauyi a Algeria.
Masu zanga-zangar neman sauyi a Algeria. AFP - RYAD KRAMDI

Gwamnatin Algeria dai ta shafe kusan shekaru 2 tana fama da zanga-zangar neman sauyi karkashin kungiyar Hirak da dubban ‘yan kasar suka kafa domin kawar da gwamnatin tsohon shugaban kasar AbdulAziz Bouteflika, bayan da yayi yunkurin zarcewa bisa shugabancin kasar karo na 5 a jere cikin shekarar 2019.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.