Isa ga babban shafi
SAHEL-TA'ADDANCI

Babu inda 'Yan ta'adda suka mallaki manyan makamai kamar Sahel - Bazoum

Shugaban Jamhuriyar Nijar Bazoum Mohammed ya bayyana cewar ba karamar kuskure akayi ba wajen gaza dakile safarar makaman dake fitowa daga kasar Libya wadanda ‘Yan ta’adda ke amfani da su wajen kai munanan hare hare a Yankin Sahel.

Shugaba Bazoum lokacin jawabi ga taron tsaro na Darkar
Shugaba Bazoum lokacin jawabi ga taron tsaro na Darkar © Niger Presidency
Talla

Bazoum yace kasashen Sahel na bukatar taimako daga kawayen su na duniya wajen tattara bayanan asiri da jiragen yaki da kuma horar da jami’an tsaro domin tinkarar matsalar tsaron da ta addabi yankin.

Dangane da batun tattara bayanan asiri, shugaban Nijar yace babban kuskuren abokan aikin su shine rashin sanya hannu wajen yaki da safarar makaman dake fitowa daga Libya, abinda ya bayyana shi a matsayin babban ginshikin rura wutar hare haren ta’addanci.

Shugaba Bazoum Mohammed da Cyril Ramaphosa da Macky Sall
Shugaba Bazoum Mohammed da Cyril Ramaphosa da Macky Sall © Niger Presidency
Yanzu haka sojojin kasashen Sahel da wasu kasashen Turai cikin su harda Faransa na fafatawa da ‘Yan ta’adda a Yankin wajen dakile hare haren da suke kaiwa.

Shugaban yace kungiyoyin ‘Yan ta’addan dake kai hare hare a Yankin Sahel sun banbanta sakamakon kazaman makaman da suke dauke da shi, wadanda suke samu cikin sauki daga masu safarar su daga kasar Libya.

Bazoum yace wani lokaci ya kan yi tunanin cewar wasu makaman da ‘Yan ta’addan ke dauke da shi ya zarce na sojoji, musamman ganin irin samfurin makaman harba makamin roka da ake kira RPG da kuma bindigogi masu sarrafa kan su da ake kira M80 da suka mallaka.

Shugaba Macky Sall lokacin jawabin bude taro
Shugaba Macky Sall lokacin jawabin bude taro © Niger Presidency
Shugaban yace babu wani yanki na duniya da ‘Yan ta’adda suka mallaki irin wadannan kazaman makamai kamar yadda suke da shi a yankin Sahel.

Tun daga shekarar 2011 lokacin da aka kashe shugaban Libya Muammar Ghadafi kasar ta fada cikin rudani da tashin hankali da kuma rikicin kabilancin wanda wani lokaci kasashen ketare ke rura wutar sa.

Bazoum yace tumbatsar makaman kasar zuwa yankin Sahel ya taimakawa ‘Yan ta’adda tare da wasu kungiyoyin ‘Yan bindiga wadanda ke aikata manyan laifuffuka kamar yadda ake gani yau a Najeriya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.