Isa ga babban shafi
Somalia

Rikici tsakanin jami'an tsaro a Somalia ya raba daruruwan iyalai da gidajensu

Kazamin rikici tsakanin bangarori biyu na jami'an tsaro da ke gaba da juna a birnin Bosaaso mai tashar jiragen ruwa a Somalia, ya tilastawa daruruwan iyalai barin gidajensu.

Wani yankin na lardin Putland mai cin gashin kansa dake kasar Somalia.
Wani yankin na lardin Putland mai cin gashin kansa dake kasar Somalia. Getty Images - Yannick Tylle
Talla

Jami’ai sun ce an kwashe kwanaki ana gwabza kazamin fada a birnin na Bosaaso, hedkwatar kasuwancin jihar Puntland mai cin gashin kanta a arewa maso gabashin kasar ta Somalia.

Wani jami'in yankin, Abdirizak Mohammed ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa, har yanzu ba a san takamaiman adadin mutanen da suka rasa muhallansu ba a garin da ke gabar tekun Bahar Rum, amma tabbas yawansu ya kai daruruwa.

A ranar Alhamis din da ta gabata hukumar kula da jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya OCHA ta ce ta damu matuka game da karuwar tashe-tashen hankula a birnin na Bosaaso.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.