Isa ga babban shafi
Burkina Faso

Dubban 'yan Burkina sun yi zanga-zangar goyon bayan juyin mulki

Magoya bayan sojojin da suka gudanar da juyin mulki a kasar Burkina Faso sun gudanar da zanga zangar nuna musu goyon baya kan kawar da zababbiyar gwamnatin kasar, a daidai lokacin da kungiyar kasashen Afirka ta Yamma da Majalisar Dinkin Duniya ke adawa da matakin.

Wasu 'yan Burkina Faso a birnin Ouagadougou, yayin zanga-zangar nuna goyon baya ga sojojin da suka yi juyin mulki.
Wasu 'yan Burkina Faso a birnin Ouagadougou, yayin zanga-zangar nuna goyon baya ga sojojin da suka yi juyin mulki. AFP - OLYMPIA DE MAISMONT
Talla

Daruruwan magoya bayan sojin ne suka shiga gangamin da aka yi a dandalin kasa da ke tsakiyar birnin Ouagadougou inda suke dauke da tutar kasar suke kuma busa sarewa da bayyana goyan bayan su ga shugabannin sojin.

'Yan kasar Burkina Faso a birnin Ouagadougou, yayin murnar kifar da gwamnatin shugaba Roch Marc Christain Kabore da sojoji suka yi. 24 ga Janairu, 2022.
'Yan kasar Burkina Faso a birnin Ouagadougou, yayin murnar kifar da gwamnatin shugaba Roch Marc Christain Kabore da sojoji suka yi. 24 ga Janairu, 2022. © AFP/Olympia de Maismont

Daya daga cikin masu shirya gangamin Lassane Ouedrago ya ce sun dade suna kira ga shugaban Christian March Kabore da ya sauka daga kujerarsa saboda gazawa wajen magance kashe kashen da ake yi a cikin kasar amma yaki.

A ranar Litinin, Jami’an sojin Burkina Faso suka kama shugaban kasar Roch Marc Christian Kabore, wanda ya sha fuskantar zanga-zangar adawa daga dubban jama’a akan gazawarsa wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda a kasar.

A halin yanzu dai kasar da ke yankin Sahel tana karkashin kungiyar sojoji ‘yan Kishin Kasa ta MPSR, wadda  Laftanar-Kanar Paul-Henri Sandaogo Damiba ke jagoranta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.