Isa ga babban shafi

Sojojin Algeria guda 2 sun mutu lokacin artabun da suka yi da ‘Yan ta’adda

Ma'aikatar tsaron Algeria ta sanar da cewar sojojin ta guda 2 sun mutu lokacin artabun da suka yi da ‘Yan ta’adda kusa da iyakar Nijar, yayin da suma suka kashe biyu daga cikin su.

Masu aikin ceto a yankin TIZZI oUZOU
Masu aikin ceto a yankin TIZZI oUZOU AFP - RYAD KRAMDI
Talla

Sanarwar sojin ta ce anyi arangamar ce a yankin Hassi Tiririne dake kusa da Jamhuriyar Nijar. Sojojin Algeria na yawan bada irin wadannan sanarwar hallaka Yan ta’adda shekaru 20 bayan kawo karshen yakin basasar kasar wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane sama da 200,000.

Taswurirar kasar Algeria
Taswurirar kasar Algeria © Latifa Mouaoued

Duk da yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla a shekarar 2005 na kawo karshen tashin hankalin, Yan bindiga na ci gaba da kai hare hare akan jami’an tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.