Isa ga babban shafi

Senegal ta shirya don kawar da kungiyar Burkina Faso a Kamaru

A  yau laraba  kungiyar kwallon kafar Senegal za ta fafata da kungiyar kwallon kafar Burkina Faso a wasar daf da na karshe a birnin Yaounde.Wannan dai ne karo na biyar da kungiyar kwallon kafar Senegal ke kaiwa wannan mataki, yayinda Burkina Faso ke cimma wannan mataki  sau hudu a tarihi.

Wasu daga cikin magoya bayan kungiyar kwallon kafar Senegal
Wasu daga cikin magoya bayan kungiyar kwallon kafar Senegal CHARLY TRIBALLEAU AFP
Talla

A shekara ta 2013 kungiyar kwallon kafar Burkina Faso ta kai mataki na karshe,inda kungiyar kwallon kafar Najeriya ta lallasa ta da ci 1 mai ban haushi.

Yan wasan Senegal
Yan wasan Senegal AFP PHOTO / ISSOUF SANOGO

Mai horar da kungiyar kwallon kafar Burkina Faso Kamou Malo yayin tattaunawa da manema labarai a kasar ta Kamru ya jaddada cewa kam a wannan karo ,ya na yekini n za su fice wannan mataki zuwa wasar karshe.Babu shaka Burkina Faso za ta lashe wannan kofi.

Yan wasan Burkina  Faso
Yan wasan Burkina Faso © AFP

Kazalika yan wasan Senegal  na sa ran kafa tarihi a wannan karo.

Yan wasan Senegal da suka hada da Abdou Diallo dan wasan baya, Sadio Mane dan wasan gaba, ‘wannan karo kam sun shirya don ganin sun koma da wannan kofi a gida’.

Mai horar da kungiyar kwallon kafar Senegal Aliou Cisse babu shaka ,zuwan su kasar ta Kamaru da shirin lashe wannan kofi ne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.