Jam'iyyar Barrow ta lashe kujerun majalisar Gambia 19 cikin 53
Jam’iyyar shugaban kasa Adama Barrow a kasar Gambia ta lashe kujeru 19 daga cikin 53 dake Majalisar dokokin kasar abinda zai tilasata masa kulla kawance kafin jagorancin majalisar.
Wallafawa ranar:
Talla
Wannan sakamako ya nuna cewar Jam’iyyar NPP ta shugaban ya kawar da jagorancin da Jam’iyyar UDP ke da shi a majalisar da ta shude.
Kundin tsarin mulki ya baiwa shugaban kasa damar nada ‘Yan majalisu guda 5 tare da shugaban majalisar wanda ake saran ya zaba nan da yan kwanaki masu zuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu