Isa ga babban shafi
Somalia

An sanya dokar takaita zirga-zirga a Somalia gabanin zabe

A yau Asabar ‘yan sanda a Somalia suka sanar da ayyana dokar takaita zirga zirga a babban birnin kasar Mogadishu, tana mai bayyana fargabar tabarbarewar tsaro bayan da ta haramta duk wasu sabogogi na al’umma har zuwa kammala kada kuri’a a zaben shugaban kasar a gobe Lahadi.

Shugaban Somalia. Mohamed Abdullahi Farmajo.
Shugaban Somalia. Mohamed Abdullahi Farmajo. AP - Farah Abdi Warsameh
Talla

Gwamman ‘yan takara ne ke fafatwa a wannan zabe a kasar da ke fama da matsalar ‘yan ta’adda masu ikirarin jihadi, a yayin da take fama da barazanar yunwa.

Kakakin ‘yan sandan kasar Abdifatah Adan ya bayyana a wani taron manema labarai cewa daga yau Asabar da karfi 9 dacrabi na dare za a takaita zirga zirgar ababen hawa da mutane.

Tuni kawayen Somalia na kasa  da kasa suka shaida wa hukumomin kasar cewa jinkirta zaben  da aka yi sakamakon dambarwar siyasa yana da hadari ganin yadda ya dauke hankali daga yaki da kungiyar ‘yan ta’adda ta Al-Shabaab, mai ikirarin jihadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.