Isa ga babban shafi

Majalisar dokokin Somalia ta amince da nadin sabon Firaminista

Majalisar dokokin Somalia ta amince da nadin Hamza Abdi Barre a matsayin sabon Firaministan kasar, matakin da ya share fagen kafa sabuwar gwamnati a  kasar dake yankin kuryar gabashin Afirka.

'Yan majalisar dokokin kasar Somalia.
'Yan majalisar dokokin kasar Somalia. © REUTERS/Feisal Omar
Talla

Dukkanin ‘yan majalisa 220 da suka halarci zaman da aka yi a jiya Asabar ne suka tabbatar da nadin Firaminista  Barre, inda kuma yayi rantsuwar kama aiki.

Sabuwar gwamnatin Somalia na fuskantar kalubale ta fuskokin tattalin arziki da tsaro, da suka hada da, bala’in yunwa da kuma barazanar kungiyar Al Shebaab dake hankoron kifar da gwamnati.

A baya bayan nan wani rahoton majalisar dinkin duniya ya bayyana cewar, kimanin 'yan Somalia miliyan 7 da dubu 100, kusan rabin al'ummar kasar, na fama da yunwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.