Ganduje ya nemi gafara a wurin Kanawa
Gwamnan Jihar Kano dake Najeriya, Abdullahi Umar Ganduje ya bukaci jama’ar jihar da su masa aikin gafara, musamman wadanda ya batawa lokacin mulkinsa.
Wallafawa ranar:
Ganduje wanda ya bukaci gafarar lokacin da ya halarci wajen tafsiri a Masallachin Al-furqan dake birnin Kano, yace ganin wa’adin mulkinsa yazo karshe, yana bukatar jama’ar jihar su yafe masa, kuma shima ya yafewa duk wanda ya saba masa.
Gwamnan yayi amfani da wannan dama wajen ban kwana da jama’ar jihar da kuma musu fatan alkhairi ganin cewar a ranar 29 ga watan gobe zai mika mulki ga Abba Kabir na Jam’iyyar NNPP wanda ya samu nasara a zaben da akayi a watan jiya.
Ganduje ya kwashe shekaru 8 a karagar mulki a matsayin zababben gwamnan jihar Kano, bayan shekaru 8 da yayi yana yiwa Dr Rabiu Musa Kwankwaso mataimakin gwamna.
Masana siyasa na kallonsa a matsayin daya daga cikin wadanda suka kwashe dogon lokaci a sha’anin mulkin jiha, kuma daya daga cikin wadanda gwamnonin da suka yi aiki da su suka baiwa kujerar gwamna sabanin yadda ake gani a siyasar Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu