Isa ga babban shafi

Najeriya: Ana gudanar da zabukan cike gurbi a jihohi 24 na kasar

A Najeriya, yau Asabaar  ake gudanar da   zabukan cike gurbi a mazabu 2660 a kananan hukumomi 185  a cikin jihohi 24 na kasar.

Wata mata yayin kada kuri'ar yayin zaben shugaban kasa a birnin Lagos dake Kudancin Najeriya. 14/04/2007.
Wata mata yayin kada kuri'ar yayin zaben shugaban kasa a birnin Lagos dake Kudancin Najeriya. 14/04/2007. AP - SUNDAY ALAMBA
Talla

Ana gudanar da zabukan gwamna da na ‘yan majalisun dokoki a jihohin Adamawa da Kebbi, saboda haka ne ma babban sufeto janar na ‘yan sandan kasar Usman Baba, ya yi umurnin a jibge dimbim jami’an ‘yan sanda da kayan aiki don tabbatar da an gudanar da zabukan lafiya.

Hankula za su fi karkata a jihohin Adamawa, Kebbi na arewacin kasar, inda za a sake zabukan gwamnoni bayan da aka  ta ayyana su a matsayin wadanda ba su kammalu ba a zaben 11 ga watan Maris.

Za a gudanar  zaben cike bgurbbi na gwamna a mazabu 142 a fadin kananan hukumomi 20 na jihar Kebbi, kuma zai kasance aranagama tsakanin jam’iyyar APC  da na PDP ne.

Aayyana zaben da aka yi tun da farko a jihar a matsayin wanda bai kammalu ba, biyo bayan soke sakamakon zabe  kananan hukumomi 20 daga cikin 21 na jihar.

Kafin ayyana zaben a matsayin wanda bai kammalu ba, dan takarar jam’iyyar APC, Dokta Nasir Idris nne ke kan gaba da kuri’u, 388,258 a yayin da Janar Aminu Bande  na jam’iyyar PDP ke biye da kuri’u 342,980.

A jihar Adamawa, za a gudanar da zaben cike gurbi a kanana hukumomi 20 don tabbatar da wanda zai dare  kujerar gwamnan jihar a tsakanin gwamna mai ci, Ahmadu Fintiri na jam’iyyar PDP da Sanata Aishatu Binani ta jam’iyyar APC.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.