Isa ga babban shafi

Marocco ta ceto bakin haure sama da 50 dake kokarin shiga Spain

Sojojin ruwan kasar Morocco sun kama bakin haure sama da 50 daga yankin kudu da hamadar sahara a gabar tekun kudancin kasar, a daidai lokacin da ake samun karuwar kwararar ‘yan ciranin zuwa kasar Spain.

Wasu daga cikin bakin haure da ke neman zuwa Turai ta tekun Libya
Wasu daga cikin bakin haure da ke neman zuwa Turai ta tekun Libya Taha JAWASHI / AFP
Talla

Kamfanin dillancin labaran MAP ya ruwaito majiyar sojan kasar, ta na cewa, "Rundunar sojojin ruwa ta Royal da ke sintiri a kusa da Tan-Tan a ranar Talata sun taimaka wa bakin haure 56 da ba su samu damar tsallakawa ba daga yankin kudu da hamadar Saharar Afirka a cikin wani karamin kwale-kwale."

Sanarwar rundunar sojin Morocco tace, bakin hauren "sun sami agajin farko a cikin jirgin, kafin a kwashe su cikin koshin lafiya zuwa tashar jiragen ruwa na Tan-Tan, sannan a mika su ga jami'an tsaron Jandarma domin gudanar da ayyukan da suka saba".

A ranar Litinin din da ta gabata ne dai rundunar tsaron gabar ruwan Morocco ta sanar da gano gawarwakin wasu 'yan ci-rani biyar 'yan kasar Senegal tare da ceto wasu 189 da kwale-kwalen su ya kife a ranar Asabar a kusa da Guerguerat da ke yammacin Sahara a kudancin kasar Morocco.

Akalla bakin haure 'yan kasar Senegal 13 ne suka mutu a tsakiyar watan Yuli lokacin da jirginsu ya nutse a gabar tekun Morocco, a cewar hukumomin kasar Senegal.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.