Isa ga babban shafi

Jam'iyyun siyasa na shirin kalubalantar Sojin Mali a gaban kotun kolin kasar

Kungiyoyin fararen hula da jam’iyyun siyasa a Mali sun bukaci kotun koli kan ta umarci gwamnatin sojin kasar da ta dakatar da haramcin da ta yi game da gudanar da harkokin siyasa. 

Shugaban mulkin Soji na Mali Kanal Assimi Goita.
Shugaban mulkin Soji na Mali Kanal Assimi Goita. © AP
Talla

A wata sanarwa da suka fitar, kungiyoyin fararen hular da jam’iyyun siyasa da ke adawa da umarnin Sojojin, sun yi korafi ga babbar kotun kasar ta Mali, suna neman a soke hukuncin da suke ganin take hakkin Dan-Adam ne.

Tun a shekarar 2021 ne sojoji a Mali suka yi juyin mulki karo na biyu, inda suka yi alkawarin gudanar da zabe a watan Fabrairun daya gabata tare da maida mulki ga farar hula tun a watan Maris.

Sai dai mahukuntan kasar sun dage zaben a watan Satumbar bara saboda wasu dalilai, yayinda har zuwa yanzu basu sanar da dalilin gaza zaben na watan Maris ba.

Tashe-tashen hankula a kasar ta Mali na ci gaba karuwa, sakamakon gaza cika alkwarin gudanar da zabe da sojojin da ke mulkin kasar su ka yi a baya.

Lamarin da masu fafutuka ke kallon sa a matsayin koma baya ga dimokradiyya a kasashen yammaci da tsakiyar Afirka, inda aka yi juyin mulki takwas cikin shekaru hudu da suka gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.