Isa ga babban shafi

Manyan jam'iyyun adawar Togo sun ce za su tirjewa sabon ƙundin tsarin mulki

Manyan jam'iyyun adawa a Togo sun bayyana shirin turjewa tare da tsayin daka wajen daukar matakai masu tsauri kan sabon kundin tsarin mulkin kasar da ya sharewa shugaban kasar hanya.

Shugaban ƙasar Togo Faure Gnassingbe. 9/04/21
Shugaban ƙasar Togo Faure Gnassingbe. 9/04/21 © Lewis Joly/AP
Talla

Yayin wani taron manema labarai da suka shirya a hedkwatar jam'iyyar PT dake Lomé, babban birnin kasar sun ce tsugune bai kare ba kan wannan batu.

Sanarwar bayan taron ta ce duk da gagarumar zanga-zangar da al'umma masamman kungiyoyin farar hula da 'yan adawa suka yi, shugabannin kasar sun ci gaba da fifita bukatunsu maimakon na al'umma.

Sabon ƙundin tsarin mulki

A ranar 6 ga watan Mayu, shugaban kasar Faure Gnassingbe ya sanya hannu kan sabon kundin tsarin mulkin da 'yan majalisar suka amince da shi a karatu na biyu a ranar 19 ga Afrilu, wanda ke tabbatar da cewa zai ci gaba da mulki bayan gagarumin nasarar da jam'iyyarsa ta Union for the Republic ta samu a zabukan 'yan majalisa da na yanki da ya gudana ranar 29 ga watan Afrilu.

A karkashin wannan gyara na kundin tsarin mulkin kasar, yanzu yan majalisu ne zasu zabi shugaban kasa maimakon zaben gama-gari daga al'umma.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.