Isa ga babban shafi
Syria

An bukaci kungiyar Larabawa ficewa daga Syria

Majalisar da ke Ba kungiyar kasashen Larabawa shawara, ta bukaci kungiyar ta janye wakilan ta dake sa ido a Syria, saboda tashin hankalin da ake cigaba da samu. Kakakin Majalisar kungiyar, Salim al Diqbassi, ya bukaci Sakatare Janar na kungiyar, Nabil al Arabi, da ya gaggauata janye wakilansu masu aikin sa ido a cikin kasar, saboda yadda ake ci gaba da kashe fararen hula.

wakilan kasashen Larabawa a kasar Syria inda suke aikin sa ido a cikin kasar
wakilan kasashen Larabawa a kasar Syria inda suke aikin sa ido a cikin kasar REUTERS/Sana/Handout
Talla

Yanzu haka mutane 286 ne aka kashe tun fara ziyarar wakilan kasashen a ranar 23 ga watan Disemba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.