Isa ga babban shafi
Pakistan

Adadin mutanen da su ka mutu a gobarar Pakistan ya haura 310

Hukumomin Kasar Pakistan sun ce adadin ma’aikatan kamfanin yin takalman da suka rasu sakamakon hadarin gobara, ya haura 310, abinda ya dada jefa shakku kan kare lafiyar ma’aikata.

Iyalan wasu da su ka tsira daga gobarar suna tayasu murna
Iyalan wasu da su ka tsira daga gobarar suna tayasu murna Reuters
Talla

Shugaban jami’an kashe gobarar Lahore, Ehtesham Salim, ya ce masu kamfanin sun kulle daukacin kofofin shiga ma’aikatar ne, dan zargi sata da suka ce ana musu, abinda ya sa ma’aikatan suka kasa tsira daga gobarar.

Babban jami’in gwamnatin Karachi, Roshan Shaikh, ya ce adadin na iya karuwa.

A yanzu haka an shigar da kamfanin da jami’an gwamnati karar aikata kisa.

Har izuwa yanzu ba a ga inda masu kamfanin su ke kuma ‘Yan sanda na nan na nemansu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.