Isa ga babban shafi
Pakistan

Harin Bom ya kashe mutane 23 a Pakistan kafin Taron D8

Wani harin kunar bakin wake da aka kai ga mabiya akidar Shi’a ya kashe mutane 23 a Pakistan a dai dai lokacin da shugabannin kasashe Takwas ke shirin gudanar da taron bunkasa tattalin arzikinsu a birnin Islamabad.

Wani Jami'in kungiyar agaji kusa da wajen da aka kai wa 'Yan Shi'a hari a Rawalpindi
Wani Jami'in kungiyar agaji kusa da wajen da aka kai wa 'Yan Shi'a hari a Rawalpindi REUTERS/Sohail Shahzad
Talla

‘Yan sandan Pakistan sun ce an kai harin ne a Rawalpindi da ke kusa da babban birnin Pakistan inda Mabiya Shi’a ke shirin gudanar da bukin Ashura da Tasu’a a watan Muharram.

Kungiyar Taliban a Pakistan ta fito da dauki alhakin kai harin bayan tayar da wani Bom kusa da masallacin mabiya Shi’a a Karachi.

A yau ne dai shugabannin kasashe guda Takwas za su gudanar da Taron bunkasa tattalin arzikinsu da suka hada da Najeriya da Iran da Turkiya da Masar da Bangladash da Indonesia.

Sai dai Rahotanni sun ce akwai tsauraran matakan tsaro da Pakistan ta dauka saboda karbar bakuncin Taron a Islamabad

Shugaban Masar Muhammed Morsi yace zai kauracewa taron a Pakistan domin sa ido wajen ganin yarjejeniyar tsagaita wuta ta zauna tsakanin Hamas da Isra'ila.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.