Afghanistan
‘Yan kungiyar Taliban sun kashe ‘Yan sanda uku a Kabul
Wasu ‘yan kunar bakin wake daga kungiyar Taliban sun kai hari kan wani ofishin ‘Yan sanda dake birnin Kabul, inda suka kashe ‘Yan sanda uku a sanyin safiyar yau Litinin. Tuni dai kungiyar ta dauki alhakin kai harin, wanda yasa dakarun tsaro na NATO suka kwashe sa’oi suna arangama da ‘yan kunar bakin waken.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotannin na nuna cewa, akalla an kashe uku daga cikin biyar na ‘yan kungiyar, a yayin da biyu daga cikinsu suka boya a wani gini suna harbin mutane.
Daga baya kuma, an kashesu, kamar yadda rahotanni suka nuna.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu