Iran ta bukaci hadin kan yankin Gulf domin tunkarar ta'addanci
Ministan kasashen wajen Iran Muhammad Javad zarif, ya yi kira ga kasashen yankin Gulf da ke makwabta da Iran, da su hada kai wajen tunkara ayyukan ta’addanci da ke neman zama babban barazana a yankunansu.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A zantawarsa da manema labarai bayan ganawa da hukumomin kasar Kuwait a ziyarar sa ta farko bayan Iran ta cimma yarjejeniyar shirin Nukiliyar kasar ta da manya kasashen duniya, Javad Zarif ya ce zaman lafiya ba ya samuwa har sai an samu haddin kan shugabannin.
Wannan dai na zuwa ne bayan Iran ta musanta wannan zargi da ake yi mata na kama wani dan kasarta a Bahrain dauke da makamai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu