Pakistan-India
Pakistan ta Saki Masunta 86 'Yan kasar Indiya
Yau Lahadi, Kasar Pakistan ta sanar da sakin wasu masunta 86 ‘yan kasar India da take tsare da su saboda yin sana’arsu a harabar tekun Pakistan.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban Gidan yari na Malir dake garin Karachi, Raja Mumtaz ya gaskata haka a tattaunawa da kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP.
Ya fadi cewa har yanzu akwai wasu mutane 363 da ake tsare da su a gidan yari.
Masunta na kasashen biyu kan fuskanci irin wannan matsala na kame a lokacin da suke kamun kifi a yankin ruwa na juna.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu