Isa ga babban shafi
Iraqi

IS ta kashe 'yan Shi'a a Iraqi

Wani sabon harin ta’addanci da kungiyar IS ta kai  kan 'yan Shi'a a birnin Bagadaza na Iraqi, ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 30 tare da jikkata fiye da 50.

IS ta zafafa kai hare hare a birnin Bagadaza tun bayan da dakarun Iraqi suka karbe garin Fallujah daga hannun mayakanta
IS ta zafafa kai hare hare a birnin Bagadaza tun bayan da dakarun Iraqi suka karbe garin Fallujah daga hannun mayakanta REUTERS/Khalid al Mousily
Talla

An kai harin kunar bakin waken ne  a raudar Sayyidi Mohammed da ke Balad kuma wuri da 'yan shi'a ke girmamawa.

Wannan dai na zuwa ne mako guda bayan mummunan harin ta'addancin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 300 da kungiyar IS ta dauki nauyin kai wa a birnin Bagadaza, harin da aka danganta a matsayin mafi muni da kasar ta gamu da shi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.