Iraqi
IS ta kashe mutane 125 a Bagadaza
Akalla mutane 125 ne suka rasa rayukansu yayin da 150 suka jikkata sakamakon wani kazamin harin kunar bakin wake da kungiyar IS ta dauki alhakin kaddamarwa a birnin Bagadaza na kasar Iraqi.
Wallafawa ranar:
Talla
Jami’an ‘yan sanda sun ce, wata mota ce makare da bama-bamai ta tarwatse a wata unguwa mai cike da hada-hadar jama’a a yankin Karrada na Bagadaza.
Rahotanni sun ce, an kai harin ne a dai dai lokacin da jama’a ke kan ganiyar gudanar da harkokin kasuwanci saboda azumin Ramadan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu