Isa ga babban shafi
Japan

Harin wuka ya kashe mutane 19 a Japan

Wani tsohon ma’aikacin gidan kula da masu fama da tabin hankali a kasar Japan ya kashe mutane 19 a gidan bayan ya daddaba musu wuka.

Jami'an tsaro sun halarci gidan da matashin ya kai harin wukar tare da kashe mutane 19 a Japan
Jami'an tsaro sun halarci gidan da matashin ya kai harin wukar tare da kashe mutane 19 a Japan 路透社
Talla

Mutumin mai shekaru 26 ya kai kan sa ofishin 'yan sanda inda ya ce, shi ne ya yi aika aikan, sannan kuma ya ce, bai kamata a rika ganin masu fama da makasa ba.

Hukumomin kasar sun bayyana maharin a matsayin Sastoshi Uematsu wanda ya yi aiki a gidan kafin a kore shi a watan Fabarairu.

Wannan harin dai ya tayar da hankulan al'ummar Japan ganin cewa, ba a cika samun irin wannan farmakin da ke lakume rayuka da dama ba a kasar wadda aka bayyana a matsayin daya daga cikin kasashen duniya da suka fi samun zaman lafiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.