AFGHANISTAN
Taliban ta dau alhakin hare-hare a Kabul
Kungiyar Taliban ta dauki alhakin jerin hare haren bama baman da aka samu a kasar Afghanistan wadanda suka hallaka mutane 24 suka kuma raunana wasu 91.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Kakakin kungiyar Taliban Zabihullah Mujahid ya ce harin farko sun kai shi ne kan ma’aikatar tsaro, yayin da na biyu kuma suka kai kan 'yan Sanda.
Wannan shine kazamin hari na uku a cikin watanni uku da suka gabata a kasar, na baya bayan nan shine harin da aka kai Jami’ar Kabul wanda ya kashe mutane 16.
Taliban na ci gaba da sanadi salwantar da rayuka a Afghanistan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu