Isa ga babban shafi

Yemen: Mutane 5,000 sun rasa muhallansu a Hodeida

Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla iyalai 5000, sun rasa muhallansu a Yemen, sakamakon hare-haren da dakarun kawance na Larabawa karkashin jagorancin Saudiyya suka kaddamar, don kwace birnin Hodeida mai tashar jiraren ruwa daga ‘yan tawayen Houthi.

Daya daga cikin motocin mayakan Houthi da hare-haren dakarun Saudiya suka lalata, a yankin al-Fazah da ke lardin Hodeida a kasar Yemen.
Daya daga cikin motocin mayakan Houthi da hare-haren dakarun Saudiya suka lalata, a yankin al-Fazah da ke lardin Hodeida a kasar Yemen. AFP
Talla

A ranar Larabar makon jiya ne, rundunar dakarun kawancen Larabawan karkashin Saudiyya ta kaddamar da sabbin hare-haren.

Majalisar dinkin duniya ta ce tun daga ranar 1 ga watan Yuni kimanin iyalai 4, 458 suka rasa matsugunansu, yayinda hare-haren ya lalata musu gidaje da gonaki.

Majalisar ta kara da cewa yanzu haka akwai fiye da mutanen miliyan 22 a kasar ta Yemen da ke bukatar agajin gaggawa ciki har da wasu miliyan 8 da rabi, da ke cikin hadarin fuskantar tsananin Yunwa.

A alhamis din da ta gabata ne kwamitin tsaron MDD ya gudanar da zama na musamman a asirce kan rikicin na Yemen, inda kasashe suka bayyana fargabarsu dangane da yiwuwar samun cikas a ayyukan jinkai ga milyoyin mutanen kasar, lura da cewa mafi yawan kayayyakin agaji ana shigar da su ne daga tashar ruwan garin na Hodeida.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.