Isa ga babban shafi
Afghanistan

Yawan wadanda suka mutu a tagwayen hare-haren Afghanistan ya kai 56

Jami’an lafiya sun ce, yawan wadanda suka mutu a tagwayen hare-haren ta’addancin da a ranar talata, aka kaiwa birnin Kabul da yankin Nangahar a Afghanistan ya karu zuwa mutane 56.

Harabar asibitin da mahara suka halaka mutane 24 a Kabul, babban birnin kasar Afghanistan. 12/5/2020.
Harabar asibitin da mahara suka halaka mutane 24 a Kabul, babban birnin kasar Afghanistan. 12/5/2020. STR / AFP
Talla

A talatar da gabata ne wasu mahara suka kutsa kai cikin wani asibiti a Kabul, baban birnin Afghanistan inda suka halaka mutane 24 ciki harda jarirai 2, kafin daga bisani jami’an tsaro suyi nasarar kashe ‘yan bindigar.

Har zuwa wannan lokaci kuma, babu wani ko wata kungiya da tayi ikirarin kai harin, sai dai shugaba Ashraf Ghani na zargin kungiyoyin Taliban da kuma ISIS.

A Nangahar dake gabashin kasar kuwa, dan kunar bakin wake ne ya tarwatsa damarar bam din dake jikinsa a tsakiyar mutanen dake halartar jana'izar wani babban jami’in dan sanda, tuni kuma kungiyar ISIS ta dauki alhakin harin da yayi sanadin halakar rayuka 32, gami da jikkata wasu 132.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.