Kakkarfar guguwa hade da ruwan sama ta hallaka mutane a India
Ruwan Sama mai karfi tare da guguwa mai tsananin gudu sun afkawa gabashin India wanda shi ne irin sa na biyu da aka samu a kasar, abinda ya tilastawa mutane sama da miliyan guda da dubu 200 tserewa daga gidajen su domin neman mafaka.
Wallafawa ranar:
Rahotanni na nuna cewa zuwa yanzu mutane akalla 3 suka rasa rayukansu sanadiyyar ibtila'in wanda hukumomin kasar suka sanar da daukar matakan hana yawaitar mace mace.
A makon jiya irin wannan guguwa tayi sanadiyar mutuwar akalla mutane 155 a Yammacin India, bayan da ta kada itatuwa da turakun lantarki da na sadarwa da kuma kwace rufin gidaje.
Masana kimiya da dama na danganta matsalar da ake yawan samu a Yankin na India da yadda dumamar yanayi ke narkar da teku.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu