Isa ga babban shafi
Indiya-Ambaliya

Ana laluben wadanda suka tsira daga ambaliyar Indiya, mamata sun zarta 115

Masu aikin ceto a Indiya a na kutsawa cikin tabo mai zurfi da baraguzai, a ci gaba da kokarin da suke na gano wadanda suka saura da ransu, a yayin da adadin wadanda suka mutu sakamakon iska mai karfi da ruwan sama ya kai 115, inda aka kwashe kusan mutane dubu 100 daga yankunan da abin ya shafa.

Ambaliyar ruwa da zaftarewar kasa sun addabi yaankunan Indiya bayan mamakon ruwan sama.
Ambaliyar ruwa da zaftarewar kasa sun addabi yaankunan Indiya bayan mamakon ruwan sama. ©REUTERS/Andrew RC Marshall
Talla

An yi mamakon ruwan sama a yankin yammacin tekun Indiya a ‘yan kwanakin nan, lamarin da ya janyo bacewar gwamman mutane a kusa da babban birnin kasuwancin kasar Mumbai, ya kuma  haddasa mummunar ambaliyar ruwa da aka dade ba a gani ba a jihar Goa.

Kamfanin dillancin labaran Faransa ya ruwaito cewa,  zaftarewar kasa a kauyen  Taliye na kusa da tsauni a kudancin Mumbai, ya share ilahirin gine gine a yankin, in ban da gidaje biyu da aka gina da siminti.

Masu aikin ceto sun shafe sa’o’i  suna kokarin gano masu sauran numfashi, amma sai gawarwaki suke fiddowa daga baraguzai, lamarin da ya tada hankalin ‘yan uwa da aminai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.