Isa ga babban shafi
Afghanistan-Taliban-Sallah

'Yan Afghanistan sun gudanar da karamar Sallah a yau

Jagoran gwamnatin Afghanistan ya bayyana a bainar jama’a a karo na 2 cikin shekaru 6 a yau lahadi, inda ya shaida wa masu ibada a taron Idin salla karama cewa kungiyar Taliban ta samar da ‘yanci da tsaro tun bayan da ta karbi mulki a shekarar da ta gabata.

(FILES) In this undated file handout photograph released by the Afghan Taliban on May 25, 2016, shows the Taliban supreme leader Hibatullah Akhundzada posing for a photograph at an undisclosed location. - Afghanistan's supreme leader called again on April 29, 2022 for the international community to recognise the Taliban government, saying the world had become a "small village" and proper diplomatic relations would help solve the country's problems. (Photo by Afghan Taliban / AFP) / -----EDITORS NOTE --- RESTRICTED TO EDITORIAL USE - MANDATORY CREDIT "AFP PHOTO / AFGHAN TALIBAN" - NO MARKETING - NO ADVERTISING CAMPAIGNS - DISTRIBUTED AS A SERVICE TO CLIENTS
(FILES) In this undated file handout photograph released by the Afghan Taliban on May 25, 2016, shows the Taliban supreme leader Hibatullah Akhundzada posing for a photograph at an undisclosed location. - Afghanistan's supreme leader called again on April 29, 2022 for the international community to recognise the Taliban government, saying the world had become a "small village" and proper diplomatic relations would help solve the country's problems. (Photo by Afghan Taliban / AFP) / -----EDITORS NOTE --- RESTRICTED TO EDITORIAL USE - MANDATORY CREDIT "AFP PHOTO / AFGHAN TALIBAN" - NO MARKETING - NO ADVERTISING CAMPAIGNS - DISTRIBUTED AS A SERVICE TO CLIENTS AFP - STR
Talla

A jawabin da yake ‘yan kwanaki bayan da wani bam ya fashe a wani masallaci a Kabul, mutumin da aka gabatar a matsayin Hibatullah Akhundzada yana kewaye ne da tsatsauran tsaro.

Ya taya dimbim masu ibada a masallacin Eidgah da ke kudancin birnin Kandahar murnar da abin ya kira nasara da yanci da suka samu tun da taliban ta karbi ragamaar mulkin kasar.

Duk da cewa an samu raguwar tashin bamabamai a fadin kasar tun da ta fada hannun ‘yan Taliban a watan Agustan  shekarar da ta gabata, an samu matsalar hare haren bam a cikin makonni 2 na karshen watan Ramadan, wanda ya kare a Afghanistan a jiya Asabar.

Gwamman mutane ne suka mutu sakamakon hare haren da akasari mayakan IS suka dauki alhakin kaiwa a kan ‘yan Shi’a ko kuma Musulmi masu akidar Sufi.

Akhundzada ya gabatar da jawabinsa ne a sahun gaba na masallacin ba tare da ya waiga ya kalli al’ummar da ke bayansa ba.

Jami’an Taliban ba  su bari ‘yan jarida sun tinkare shi ba, kamar yadda wani wakilin kamfanin dillancin labaran Faransa ya ruwaito.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.