Isa ga babban shafi

Afghanistan: IS ta dauki alhakin mummunan harin bam da aka kai otel a Kabul

Kungiyar IS ta dauki alhakin harin da aka kai wani otel a tsakiyar birnin Kabul wanda ya shahara da ‘yan kasar China.

IS ta dauki alhakkin harin otel da ke sauke'yan kasuwar China a Kabul.
IS ta dauki alhakkin harin otel da ke sauke'yan kasuwar China a Kabul. via REUTERS - SOCIAL MEDIA
Talla

A ranar Litinin ne wasu mutane dauke da makamai suka bude wuta a cikin otal din, kuma jami’an tsaro sun kashe akalla ‘yan bindiga uku.

Asibitin Gaggawa na tafi da gidanka dake Kabul, wanda wata kungiya mai zaman kanta ta Italiya ke daukar nauyi, ta ce mutane  21 lamarin ya Rutsa da su, uku suka mutu  wasu 18 suka jikkata.

China, ta bakin kakakin ma’aikatar tsaron kasar, Wang Wenbin ta yi tir da harin da aka kai otel din da ke sauke akasari ‘yan kasuwar China, inda ya ce ‘yan kasar5 ssun jikkata.

Kungiyar Taliban ta yi ikirarin  bunkasa tsaro tun da ta kwace ragamar mulkin kasar a watan Agustan shekarar da ta gabata, amma har yanzu ana samun tashin bama bamai, wandanda kungiyar IS ta dauki alhakin akasarinsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.