Amurka
Obama ya dauki alhakin shan kaye a zaben 'Yan Majalisu
Shugaban Amurka ya dauki alhakin shan kayen da Jam’iyyarsa ta sha a zaben ‘Yan majalisu da aka gudanar a makon jiya. Obama ya shaidawa wata kafar talabijin ta CBS cewa sun sha kaye a zaben tare da daukar alhakin koma bayan farin jinin da Jam’iyarsa ta samu.
Wallafawa ranar:
Talla
Jam’iyyar adawa ce ta Republican dai ta samu rinayen kujeru a zaben da aka gudanar a ranar Talatar makon jiya, wanda ake ganin wannan shi ne zaben da zai auna farin jinin Jam’iyyar Demokurat ta Obama a zaben shugaban kasa da ke zuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu