WHO ta bukaci taron Paris ya tattauna kan kiwon lafiya
Hukumar lafiya ta duniya, WHO ta bukaci mahalarta taron kasa da kasa kan sauyin yanayi da za a yi a birnin Paris na kasar Faransa a wannan wata, da su mayar da hankali kan yadda za a magance matsalolin kiwon lafiya da ke da nasaba da illolin sauyin yanayi.
Wallafawa ranar:
Hukumar ta bayyana cewa matsalar dumamar yanayi ita ce babban dalilin da ke haddasa asarar dubban rayukan jama’a a duniya, lura da yadda ake samun yaduwar cututtuka daga wannan yanki zuwa wancan a cikin iska.
A shekarar bara ma hukumar ta lafiya ta fitar da wani rahoto da ke cewa matsalar ta sauyin yanayi ta yi sanadiyyar mutuwar sama da mutane milyan 7 a sassan duniya, sakamakon yadda jama’a ke shakar gurbataciyyar iska wadda a mafi yawan lokuta take dauke da cututtuka.
Hukumar ta bayar da misali da tsanantar zafi a wannan zamani wanda ya sa hatta a yankunan da ba a saba samun bullar cututtuka kamar zazzabin cizon sauro ba, a yau sun bayyana a can tare da kashe jama'a.
Misis Maria Neira, daya daga cikin manyan jami’ai a hukumar ta lafiya, ta ce domin ceto rayukan milyoyin mutane, ya zama wajibi ga mahalarta taron da za a fara a ranar 30 ga wannan wata na nuwamba a Faransa, su samar da yarjejeniya ta kasa da kasa a tsakaninsu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu