Isa ga babban shafi
Myanmar

Jagorar Democradiyya na Kasar Myanmar Na Asibiti Saboda Matsalar Ido

Jagorar masu kishin kafuwar Democradiyya a kasar Myanmar Uwargida Aung Sang Suu Kyi na kwance a wani Asibitin Idanu saboda matsalar ciwon ido da take fama dashi. 

Uwargida  Aung San Suu Kyi na gabatar da kasida a jamiar Harvard  a shekara ta 2012
Uwargida Aung San Suu Kyi na gabatar da kasida a jamiar Harvard a shekara ta 2012 Reuters/Jessica Rinaldi
Talla

‘Yar shekaru 70, kafofin labaran kasar sun nuna ta a Asibiti, wani likita mai suna Tin Myo Win na duba lafiyar idanun ta, kuma shine ke cikin mutane ‘yan kalilan da sojan kasar suka bari ya rika ziyartar ta a lokacin da take tsare a gidan ta na tsawon shekaru 15.

Uwargida Aung San Suu Kyi na rike da mukamin Ministan Harkokin kasashen waje na kasar.

Majiyoyi na cewa za’ayi mata aiki a idanun ta ranar 16 ga wannan wata da muke ciki.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.