Duterte ya bayyana Obama a matsayin ‘dan karuwa’
Shugaban Kasar Amurka Barack Obama ya soke ganawar da ya shirya yi da shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte bayan zagin da ya masa a wasu kalamai masu zafi.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Duterte kafin tashin sa zuwa wajen taron shugabanin kasashen Asia da Pacific ya ce ba zai bai wa Obama damar yi masa huduba kan kare hakkin Bil Adama ba sakamakon yakin da ya kaddamar na kashe masu safarar miyagun kwayoyi.
Shugaban na Philippines ya bayyana Barack Obama a matsayin ‘dan karuwa’ kalaman da suka sa fadar sa ta soke ganawar shugabanin biyu.
Tuni dai wannan batu ya dau hankali duniya inda ake ci gaba da mayar da martani kan kalaman Duterte.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu