Isa ga babban shafi
Iran

Iran ta sha alwashin cigaba da kasancewa cikin yarjejeniyar nukiliya

Kasar Iran ta bayyana shirinta na ci gaba da kasancewa cikin yarjejeniyar nukiliya da ke tsakaninta da kasashen yammacin Duniya ko da kasar Amurka ta fice daga cikinta.

Shugaban kasar Iran Hassan Rohani.
Shugaban kasar Iran Hassan Rohani. REUTERS/Danish Siddiqui
Talla

Shugaban kasar Iran Hassan Rouhani ya ce ba abinda zai hana Iran ci gaba da kasancewa cikin yarjejeniyar matukar sauran kasashen mahalarta tattaunawar basu fice ba.

A ranar Assabar mai zuwa ake sa ran shugaba Trump na Amurka zai fayyace wa Duniya matsayin kasar Amurka dangane da yarjejeniyar Nukiliyar Iran, da kasar Iran a baya ta sha nanatawa Amurka cewar za ta yi babbar nadama a tarihi matukar ta wancakalar da ita.

Tuni dai kasashen Birtaniya, China, Faransa, Jamus da Rasha suka janyo hankalin Amurka akan ta tsaya a yi da ita.

Ko a kwanan nan ma an ji shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron na neman sauran manyan kasashen Duniya da su sa baki kada yarjejeniyar ta kife, harma yana yi wa shugaba Trump kashedin cewar akwai yiwuwar barkewar yaki matukar Amurka ta yi sakacin lalacewar yarjejeniyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.