Isa ga babban shafi
Brazil

Shugaban Brazil ya sanya hannu kan dokar mallakar bindiga

Sabon Shugaban kasar Brazil Jair Bolsonaro ya sanya hannu kan wata doka wadda zata saukaka yadda ake mallakar bindiga a cikin kasar, matakin da masu sa ido ke kallon cewar zai dada haifar da matsalar tsaro.

Jair Bolsonaro sabon Shugaban kasar Brazil
Jair Bolsonaro sabon Shugaban kasar Brazil Reuters/路透社
Talla

Shugaba Bolsonaro yace dokar zata baiwa yan kasa na gari damar mallakar bindiga domin kare kan su daga mahara.

Kasar Brazil ta gamu da kisan kai har sau 64,000 a shekarar 2017, abinda ya mayar da kasar daya daga cikin kasashen da suka fi hadarin zama a duniya.

Wata kididdigar bankin duniya ta ce, Brazil ce kasa ta 8 a duniya da aka fi kisan kai, yayin da, hukumomin tsaron kasar suka ce a shekarar 2017 an aikata kisan gilla dubu 63 da 883 a fadin kasar.

Shugaban kasar Jair Bolsonaro da tsohon kaftin din sojin Brazil mai ra’ayin rikau, Jair Bolsonaro ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a karshen makon watan Oktoba na shekara ta 2018, in da ya doke abokin takararsa Fernando Haddad da sama da kashi 55 na kuri’un da aka kada.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.