Isa ga babban shafi
Amurka-Iran

Iran ta yi watsi da bukatar ganawa da Amurka bayan korar John Bolton

Sa’o’i kadan bayan da Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da tube John Bolton mai ba shi shawarar kan sha’anin tsaro daga mukaminsa, Donald Trump ya ce a shirye ya ke ya gana da shugaban kasar Iran Hassan Rouhani ba tare da wani sharadi ba.

Shugaba Trump na Amurka da Shugaban Iran Hassan Rohani
Shugaba Trump na Amurka da Shugaban Iran Hassan Rohani AFP
Talla

Kasar Iran ta yi watsi da bukatar Amurka na ganawa tsakanin shugaba Donald Trump da Hassan Rouhani a wajen taron Majalisar Dinkin Duniya da zai gudana a wannan wata a New York.

Jakadan Amurka a Majalisar Dinkin Duniya Majid Takht-Ravanchi yace Rouhani zai gana da Trump ne kawai idan Amurka ta kawo karshen ta’addancin kasuwancin da take yiwa kasar, wajen cire mata takunkumi.

Sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo da Sakataren Baitulmali Steven Mnuchin suka bayyana cewar shugaba Trump a shirye yake ya gana da shugaba Hassan Rouhani ba tare da gindaya sharudda ba, bayan ya kori mai bashi shawara kan harkokin tsaro John Bolton.

A watan jiya, shugaban Faransa Emmanuel Macron dake shiga tsakanin kasashen biyu, ya bayyana cewar akwai yiwuwar ganawa tsakanin bangarorin biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.