Isa ga babban shafi
Norway

An zakulo gawarwakin mutanen da laka ta binne a Norway

Masu aikin agaji sun zakulo gawar mutun na biyar da zabtarewar laka ta binne a wani kauye da ke kusa da babban birnin Norway kamar yadda jami’an ‘yan sanda suka sanar a yau Lahadi, yayin da ake ci gaba da neman karin mutane biyar da suka bace.

Yankin Ask na Norway ya dade yana fama da barazanar zabtarewar laka
Yankin Ask na Norway ya dade yana fama da barazanar zabtarewar laka ©REUTERS/Hannah McKay/File Photo
Talla

Ibtila’in ya auku ne a sanyin safiyar ranar Larabar da ta gabata, inda gidaje suka lalace har ma suka gusa daga ainihin mazauninsu a sanadiyar zabtarewar lakar a kauyen Ask mai tazarar kilomita 25 daga arewa maso gabashin babban birnin Oslo.

Tuni aka kwashe kimanin mutane dubu daya daga wannan kauye mai yawan al’umma dubu 5 domin sauya musu matsuguni saboda fargabar abin da ka iya aukuwa nan gaba, ganin cewa har yanzu ana jin alamar motsawar kasa a garin.

Jami’an agajin na amfani da karnuka da jiragen sama masu saukar ungulu wajen neman sauran mutanen da lakar ta binne.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.