Isa ga babban shafi
Iraqi - Zanga-zanga

Zanga-zanga ta barke a Karbala bayan kashe wani fitaccen mai fafutuka

Zanga-zanga ta barke a birnin Karbala dake kasar Iraqi biyo bayan kashe Ihab al-Wazni wani mai fafutuka da yayi kaurin suna wajen sukar gwamnati, lamarin da ya fusata dubban magiya bayansa da suka fantsama kan titunan don nuna bacin ransu.

Masu zanga-zanga a birnin Karbala na kasar Iraqi.
Masu zanga-zanga a birnin Karbala na kasar Iraqi. © | AFP
Talla

Wasu ‘yan bindiga haye kan babura suka harbe shi har lahira, harin da na’urorin daukar hoto suka nada.

Ko a watan Disambar shekarar 2019 sai da ta wazni ya tsallake rijiya da baya, lokacin da wasu ‘yan bindigar suka suka kashe wani abokinsa Fahem al-Tai mai fafutuka, a dai dailokacin da yake ajiye shi gida a birnin Karbala.

Kawo yanzu kimanin masufafutukar kare hakkin dan adam 30 aka kashe yayin da aka sace wasu da dama daga watan Oktoban 2019 zuwa bana a Iraqi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.