Zanga-zanga ta barke a Karbala bayan kashe wani fitaccen mai fafutuka
Zanga-zanga ta barke a birnin Karbala dake kasar Iraqi biyo bayan kashe Ihab al-Wazni wani mai fafutuka da yayi kaurin suna wajen sukar gwamnati, lamarin da ya fusata dubban magiya bayansa da suka fantsama kan titunan don nuna bacin ransu.
Wallafawa ranar:
Wasu ‘yan bindiga haye kan babura suka harbe shi har lahira, harin da na’urorin daukar hoto suka nada.
Ko a watan Disambar shekarar 2019 sai da ta wazni ya tsallake rijiya da baya, lokacin da wasu ‘yan bindigar suka suka kashe wani abokinsa Fahem al-Tai mai fafutuka, a dai dailokacin da yake ajiye shi gida a birnin Karbala.
Kawo yanzu kimanin masufafutukar kare hakkin dan adam 30 aka kashe yayin da aka sace wasu da dama daga watan Oktoban 2019 zuwa bana a Iraqi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu