Kasashen Turai na duba yuwuwar karfafa dangankata da yankin Balkan
Tarayyar Turai da shugabannin kasashen yankin Balkan suna cikin wani taro Talatar nan a birnin Tirana na Albania, don tattauna batun karfafa zumunci, a yayin da mamayar da Rasha ke yi a Ukraine ta farfado da kokarin kungiyar neman fadadawa.
Wallafawa ranar:
Kasashen na yankin Balkan da suka shafe shekaru suna jiran Tarayyar Turai ta karbe su sun bayyana takaicinsu a kan yadda har yanzu ake kan abu guda, musamman ma yadda tuni aka bai wa Ukraine da Maldova damar neman shiga kungiyar ta yammacin Turai.
Taron, wanda ya kunshi kasashen Albania, Bosnia, Montenegro, Kosovo, Arewacin Macedonia da Serbia, zai mayar da hankali ne a kan yaukaka hadin kai.
Yakin Ukraine ya dada jaddada wa Tarayyar Turai mahimmancin kara azama wajen samar da kwanciyar hankali a yakin na Balkan, don dakile rinjayen Rasha da China, wadda ta zuba makudan kudade a bangaren samar da kayayyakin more rayuwa a kasar.
Daya daga cikin mahimman batutuwan dubawa a wannan taro zai kasance tantance matakin sabuwar dangantaka tsakanin Tarayar Turai da yankin Balkan, kamar yada bayanai sukaa nuna gabnin taron.
A watan Yuli, Tarayar Turaai ta bude tattaunawa a kan bukatar da Arewacin Macedonia da Albania suka mikan a shiga kungiyar a shekarun baya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu